Luke 15

1To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa. 2Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, “Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci.”

3Yesu ya fadi wannan misali, ya ce, 4“Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa’in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba? 5Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.

6In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, ‘Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.’ 7Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa’in da tara wadanda ba su bukatar tuba.

8Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba? 9In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, ‘Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.’ 10Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala’ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba.”

11Sai Yesu ya ce, “Akwai wani mutum mai ‘ya’ya biyu maza, 12sai karamin ya ce wa mahaifinsa, ‘Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.’ Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.

13Bayan ‘yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha’a. 14Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.

15Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci. 16Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.

17Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, ‘Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa! 18Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. 19Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.’”

20Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa. 21Dan kuma ya ce masa, ‘Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.’

22Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, ‘Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa. 23Sa’annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki! 24Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.’ Sai suka fara liyafa.

25A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye. 26Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa. 27Bawan ya ce masa, ‘Dan’uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.’

28Amma dan’uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi. 29Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, ‘Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba, 30amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.

31Sai mahaifin ya ce masa, ‘Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne. Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan’uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.’”

32

Copyright information for HauULB